Acts 3

Bitrus Ya Warkar da Gurgu Mai Bara

1Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin adduʼa-da ƙarfe uku na rana. 2To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don ya yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali. 3Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi. 4Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!” 5Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.

6Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.” 7Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi. 8Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filayen haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah. 9Saʼad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah, 10sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.

Bitrus Ya Yi wa Masu Ƙallo Magana

11Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon. 12Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu: “Mutanen Israʼila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke ƙallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya? 13Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi. 14Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai. 15Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan. 16Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.

17“To, ʼyanʼuwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi. 18Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa, cewa, Kiristinsa zai sha wahala. 19Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokatan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji, 20don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku-Yesu ke nan. 21Dole ya kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. 22Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku. 23Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
M Sh 18.15, 18, 19


24“Hakika, dukan annabawa daga Samaʼila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki. 25Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’
Far 22.18; Far 26.4
26Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don ya albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”

Copyright information for HauSRK